Garban Kauye ya aike da Sakon ta’aziyyar Sarkin Gaya ga Mataimakinsa da al’ummar Masarautar Gaya

Date:

Daga Halima M Abubakar

Shugaban karamar hukumar Kumbotso Hon Hassan Garban Kauye Farawa ya nuna alhini da juyayi kan rasuwar Mai Martaba Sarkin Gaya Alhaji Ibrahim Abdulkadir, Kirmau Mai Gabas, yana mai bayyana shi a matsayin “daya daga cikin manyan sarakunan gargajiya a Arewacin Najeriya wanda ya taimaka wajen Kare martaba da kimar masarautar a idon Duniya.

Alhaji Hassan farawa ya bayyana hakan ne Cikin Wata sanarwa da Mataimakinsa na Musamman Kan harkokin yada labarai Shazali Saleh Farawa ya aikowa Kadaura24.

“Da yakl samun labarin Rasuwar ya yi matukar kaduwa, Shugaban ya lura cewa marigayi sarkin mutum ne mai Hakuri wanda ya bauta wa jama’arsa Babu son zuciya cikin sadaukarwa wanda yace za’a Dade Tarihin Kano da masarautar Bai manta Dashi ba, saboda jajircewarsa ga ci gaban yankin koyaushe.”

Farawa ya Aike da sakon Ta’aziyya ga Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje, Majalisar Masarautar Gaya, Mataimakinsa kuma Ajiyan Gaya Hon Shamsu Abdullahi Sa’id kademi da Iyalan mamacin, Da fatan Allah Madaukakin Sarki da Ya gafarta masa kurakuransa ya kyautata makwanci.

7 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...