Garban Kauye ya aike da Sakon ta’aziyyar Sarkin Gaya ga Mataimakinsa da al’ummar Masarautar Gaya

Date:

Daga Halima M Abubakar

Shugaban karamar hukumar Kumbotso Hon Hassan Garban Kauye Farawa ya nuna alhini da juyayi kan rasuwar Mai Martaba Sarkin Gaya Alhaji Ibrahim Abdulkadir, Kirmau Mai Gabas, yana mai bayyana shi a matsayin “daya daga cikin manyan sarakunan gargajiya a Arewacin Najeriya wanda ya taimaka wajen Kare martaba da kimar masarautar a idon Duniya.

Alhaji Hassan farawa ya bayyana hakan ne Cikin Wata sanarwa da Mataimakinsa na Musamman Kan harkokin yada labarai Shazali Saleh Farawa ya aikowa Kadaura24.

“Da yakl samun labarin Rasuwar ya yi matukar kaduwa, Shugaban ya lura cewa marigayi sarkin mutum ne mai Hakuri wanda ya bauta wa jama’arsa Babu son zuciya cikin sadaukarwa wanda yace za’a Dade Tarihin Kano da masarautar Bai manta Dashi ba, saboda jajircewarsa ga ci gaban yankin koyaushe.”

Farawa ya Aike da sakon Ta’aziyya ga Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje, Majalisar Masarautar Gaya, Mataimakinsa kuma Ajiyan Gaya Hon Shamsu Abdullahi Sa’id kademi da Iyalan mamacin, Da fatan Allah Madaukakin Sarki da Ya gafarta masa kurakuransa ya kyautata makwanci.

7 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...