Yanzu-yanzu: NAHCON ta tsawaita wa’adin biyan kuɗin aikin Hajjin Bana

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Hukumar kula da aikin hajji ta Najeriya NAHCON ta kara wa’adin lokacin biyan kuɗin aikin hajjin shekara ta 2024.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata, mai dauke da sa hannun mataimakiyar daraktar hukumar ta NAHCON, Fatima Sanda Usara.

Sanarwar ta ce sabon wa’adin na yanzu shi ne 31 ga Janairu, 2024, maimakon 31 ga Disamba, 2023.

Talla

Sanarwar ta ce, an kara wa’adin ne saboda yadda malaman addini, Hukumomin jin dadin jiha, Gwamnonin Jihohi, da sauran masu ruwa da tsaki suka bukata.

Wakokin Kannywood 5 Da Suka Fi Shahara A 2023

“Saboda haka, NAHCON tana da yakinin cewa kafin cikar sabon wa’adin, tare da hadin gwiwar hukumomin Jin dadin alhazai mutane zasu sami damar biyan kudin aikin Hajjin 2024,” inji ta.

Ta bayyana cewa amincewar da gwamnatin tarayya ta yi na tsawaita wa’adin zai ba da dama ga mutane su sami damar sauke faralin a bana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...