Kisan Masu Maulidi: Lauyoyin Arewa Zasu Maka gwamnatin tarayya a Kotu

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Kungiyar ‘Concerned Northern Forum’ da lauyoyi suka kafa, ta sha alwashin gurfanar da gwamnatin tarayya a gaban kotu, inda ta bukaci a biya diyya ga Iyalan wadanda harin bam na garin Tudun Biri dake karamar hukumar igabi a jihar Kaduna ya rutsa da su .

Ya zuwa yanzu an gano cewa an kashe mutanen kauyen sama da 120 yayin da suke gudanar da bikin Mauludi a daren Lahadin da ta gabata.

Da yake jawabi a madadin kungiyar lauyoyin, Barista Nafi’u Abubakar, ya bayyana cewa kungiyar zai tabbatar da cewa iyaye da yan uwan wadanda aka babu gaira babu dalili an yi musu adalci yadda ya kamata.

Talla

Nafi’u wanda ya bayyana haka yayin da yake zantawa da manema labarai a Kaduna a ranar Asabar, ya bukaci gwamnatin tarayya da ta dauki matakin gaggawa don tabbatar da gudanar da cikakken bincike kan wannan lamari.

Yace ya zama wajibi a hukunta wadanda suka aikata wannan aika-aika, sannan a samar da matakan hana sake afkuwar irin haka a nan gaba.

Gwamnan Kano Abba Kabir ya nada sabbin manyan sakatarori da Kuma sauyawa wasu wuraren aiki

“Muna kuma kira ga rundunar sojin Najeriya da ta sake duba ka’idojin aiki tare da horar da jami’anta, domin gujewa asarar rayukan mutanen da ba su ji ba ba su gani ba yayin ayyukan soji. Yana da matukar muhimmanci rundunar sojojin Najeriya a matsayinta na mai kare kasa, ta yi taka-tsan-tsan don gujewa sake samun barnar da aka samu da kuma asarar rayukan fararen hula,” inji shi.

Kungiyar mai dauke da mambobi sama da 600 sun mika sakon ta’aziyya ga iyalai da yan uwan wadanda suka rasa rayukansu a wannan mummunan lamari.

“Mun tsaya mu su akan wannan abun mara dadi da ya faru har sai mun ga anyi musu adalci. Kungiyar ‘Concerned Northern Lawyers Forum’ za ta yi aiki tukuru wajen neman hanyoyin da doka ta tanada domin neman diyyar rayukan wadanda abun ya shafa,” inji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...