Zargin bata tarbiyya: Sarkin Katsina na shirin korar AGILE daga jihar

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Mai Martaba Sarkin Katsina, Abdulmuminu Kabir, na shirin korar shirin nan na inganta ilmin ’yan mata mai suna AGILE daga fadin jihar.

Sarkin ya ce, shirin na AGILE yana wuce gona da iri da kuma kokarin gurbata tarbiyyar Musulunci da ta al’ada da aka san yankin da ita.

Sarkin ya bayyana haka ne a fadarsa ranar Asabar lokacin da yake aiwatar da wasu nade-nade.

Talla

Kazalika, ya ce shirin yana cin karo da koyarwar addinin Musulunci wanda ya ce a matsayinsu na iyayen al’umma ba za su bari hakan ta faru ba.

Don haka ya ce, lallai ne wannan shiri ya fita daga Jihar Katsina baki daya.

Hukuncin Kotun Koli: ‘Yan sanda sun yi sabon gargadi ga al’ummar jihar Kano

Shiri AGILE na da nufin habaka ilmin zamani na ’yan mata daga karamar makaratun sakandaren zuwa babba, inda ma har ake ba su wani ihisani.

Sai dai wasu masu nazari da suka yi sharhi a kai sun ce shirin in baya ga bata tarbiyya da kokarin sanya daliban bujire wa iyaye da wasu ka’idodi da tarbiyar addini da ta al’ada babu abin da shirin yake koyarwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...