Dalilin da yasa kotu ta bada umarnin rufe asusun gwamnatin Kano

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta bayar da umarnin dakatar da wasu daga cikin asusun gwamnatin jihar Kano a wasu bankunan kasuwanci guda 20 a Najeriya.

Mai shari’a I.E Ekwo ya bayar da wannan umarni ne a wata kara da masu shaguna a filin idi da kungiyar ‘yan kasuwa suka shigar a kan ruguza shagunansu da gwamnatin Kano tayi, wanda suka bayyana a matsayin haramtaccen matakin da gwamnati ta dauka a watan Yunin 2023.

Talla

Kadaura24 ta ruwaito cewa wadanda suka shigar da karar, Alhaji Awalu sai’du, Ifeanyi Nwobodo, Alhaji Sani Uba, Alhaji Abdullahi A. Idris, da wasu mutane 25 sun kai karar gwamnatin jihar Kano, a matsayin masu bin bashi, har naira biliyan 30.

Rayukan mutanen da aka kashe a taron Maulidi ya kamata lauyoyi su bi kadi ba dimokuradiyya ba – Isa Bello ja

Umarnin yana kunshe ne a cikin daftarin hukuncin da aka bayar a ranar 28 ga Nuwamba, 2023 kuma aka bai wa manema labarai ranar Larabar nan.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito babbar kotun tarayya dake Kano ta umarci gwamnatin jihar kano da ta biya diyyar Naira Biliyan 30 ga masu shagunan da aka rushe musu a filin idi ba bisa ƙa’ida ba.

Karin bayani na nan tafe…

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...