Daga Tijjani Mu’azu Aujara
Gwamnatin Najeriya ta ce har yanzu ma’aikatan wasu hukumomin gwamnatin tarayya ba su samu albashin su na watan Nuwamba ba ne, saboda hukumomin sun karar da kasonsu na kasafin kuɗin wannan Shekarar mai karewa.
Kadaura24 ta rawaito Ministan harkokin kudi, Wale Edu ne ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da manema labaran fadar shugaban kasa a Abuja.
Wasu hukumomi irin su manyan makarantun tarayya da FRCN, ba su biya ma’aikatansu albashin watan Nuwamba ba.

“Duk hukumomin da abin ya shafa sun gama kashe kudadensu na kasafin kudi kuma an rufe tsarin da yake Basu damar biyan albashin,” in ji shi
Mista Wale Edu, ya ce gibin na kunshe ne a cikin kasafin da majalisar ta amince da shi kwanan nan.
Yadda Jirgin Sojin Nigeria ya yi ruwan bam a kan masu taron Mauludi a Kaduna
Ya ce ma’aikatarsa ”kawai ta sami shawarwari game da gibin a ranar Litinin” kuma ana kokarin ganin an dawo da hukumomin kan tsarin da ya dace domin su sami damar biyan kudaden ma’aikatan na su .
Da yake karin haske kan dalilin da ya sa hukumomin suka karar da kudaden, Mista Wale Edun ya ce wasu hukumomin sun dauki karin ma’aikata ba tare da sanar da ma’aikatar kudi akan lokaci ba.
“Ya kamata hukumomin su gaya mana akan lokaci domin a dauki matakan da suka dace,” in ji ta.