Yadda Wani Kwale-kwale ya Kama da Wuta Yana tsaka da Tafiya a Ruwa a Jihar Neja

Date:

Daga Abubakar Mustapha

Rahotanni daga jihar Neja na cewa wasu mutane uku sun bace bayan da wani jirgin fasinja na katako ya kone kurmus, jim kadan bayan tashinsa a unguwar Katcha da ke karamar hukumar Katcha a jihar Neja a ranar Juma’a.

A cewar wani ganau, Abdulmalik Adamu, lamarin ya faru ne da misalin karfe 6 na yamma jim kadan bayan kwale-kwalen ya kammala lodin kaya da fasinjojin da zasu koma garuruwansu bayan kammala cin kasuwar Katcha wadda take ci mako-mako.

Talla

Ya ce matukin kwale-kwalen yana tsaka fa sarrafa injin ne sai kwale-kwalen ya kama da wuta, lamarin da ya tilasta wa fasinjoji yin tururuwar fita daga jirgin domin tsira da rayukansu.

Shirin Dadin-Kowa ya sa samari son yin wuf da ni – Fati Harka

Da yake tabbatar da faruwar lamarin ga gidan Talabijin na Channels, shugaban masu gudanar da sanar kwale-kwalen na Katcha, Dangana Mai kwale-kwale, ya tabbatar da batan mutane uku wadanda yace duk Yara ne , amma bai bayyana musabbabin tashin gobarar ba, sai dai ya ce jirgin ya kone kurmus tare da wasu kayayyaki na miliyoyin naira.

Wasu masunta daga gudanar da harkokin su a wajen sun taimaka wajen kwaso wasu daga cikin wadanda lamarin ya rutsa da su tare da gaggauta nesanta jirgin da ke konewa da wasu .

Talla

Jirgin ruwan dai ya ɗauki fasinjoji ne zuwa garuruwan Zakanti, Danbo da wasu yankuna dake gabar ruwan wadanda suke cikin kananan hukumomin Katcha da Agaie a jihar Neja.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...