Da dumi-dumi : Yan Bindiga sun sako Daliban Islamiyya na Tegina dake jihar Neja

Date:

Sama da dalibai 70 na makarantar Islamiyya da ke garin Tegina wadanda ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a jihar Neja, masu garkuwa da mutane sun sako su.

Kadaura24 ta ruwaito, an sace Daliban ne daga harabar makarantarsu tun a watan Yuni.

Wata majiyar tsaro ta shaida wa PRNigeria cewa daliban na kan hanyarsu ta zuwa Minna akan hanyar Kagara daga Birnin Gwari.

Rahotanni sun nuna Daliban Islamiyyar sun kwashe tsawon kwanaki 88 a hannun masu garkuwar .

PRNigeria tana wallafa adadi tun bayan sace daliban a Arewacin Najeriya. Daliban da aka sace na Kwalejin Gwamnatin Tarayya ta Yauri Suma sun kasance a tsare na tsawon kwanaki 70 yayin da sauran daliban da aka sace na wata Makarantar Baptist a Kaduna suka shafe kwanaki 52 a hannun masu garkuwa da mutane.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...