Da dumi-dumi : Yan Bindiga sun sako Daliban Islamiyya na Tegina dake jihar Neja

Date:

Sama da dalibai 70 na makarantar Islamiyya da ke garin Tegina wadanda ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a jihar Neja, masu garkuwa da mutane sun sako su.

Kadaura24 ta ruwaito, an sace Daliban ne daga harabar makarantarsu tun a watan Yuni.

Wata majiyar tsaro ta shaida wa PRNigeria cewa daliban na kan hanyarsu ta zuwa Minna akan hanyar Kagara daga Birnin Gwari.

Rahotanni sun nuna Daliban Islamiyyar sun kwashe tsawon kwanaki 88 a hannun masu garkuwar .

PRNigeria tana wallafa adadi tun bayan sace daliban a Arewacin Najeriya. Daliban da aka sace na Kwalejin Gwamnatin Tarayya ta Yauri Suma sun kasance a tsare na tsawon kwanaki 70 yayin da sauran daliban da aka sace na wata Makarantar Baptist a Kaduna suka shafe kwanaki 52 a hannun masu garkuwa da mutane.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Amfani da al’ada a cikin fina-finan kannywood ne ya hana masa’antar ci gaba – Khadija Osi

Jaruma a masana'antar Kannywood Khadija Muhammad wacce aka fi...

Nasarar da Ɗaliban Kano suka Samu a NECO Kokari ne na Gwamnatin Ganduje – Sanusi Kiru

Tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Hon. Muhammad Sanusi...

Gwamnatin Tarayya ta Kaddamar da Aikin samar da wutar sola na Naira Biliyan 12 a asibitin Malam Aminu Kano

Kwana biyu bayan rikicin wutar lantarki tsakanin Asibitin Koyarwa...

Kano Ta Zama Zakara A Jarrabawa NECO Ta Bana

Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta Najeriya (NECO),ta fitar...