Gwamnan Niger ya Nada Mata 131 A Matsayin Masu Taimaka Masa

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Gwamnan jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya amince da nadin mata 131 a mukamai daban-daban na siyasa a jihar.

 

Kakakin gwamnan, Bologi Ibrahim, a wata sanarwa da ya fitar jiya, ya ce 41 daga cikin wadanda aka nada za su yi aiki a matsayin kodineta yayin da sauran 90 za su kasance a matsayin manyan mataimaka na musamman ga gwamnan (SSAs).

Talla

Yayin da yake taya wadanda aka nada murna, gwamnan ya yi kira gare su da su jajirce tare da bayar da gudunmawarsu wajen samun nasarar manufofin gwamnatinsa.

Shugaban Mulkin Soji na Nijar ya bayyana lokacin da zasu mika Mulki ga farar hula

Bago ya ce nadin nasu ya zo ne domin cika alkawarin da ya yi a lokacin yakin neman zabe na baiwa mata damar ba da gudummawarsu wajen gina jihar ta Neja.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...