Likitoci sun janye yajin aikin da suke yi

Date:

Ƙungiyar lokitoci masu neman ƙwarewa a Najeriya ta janye yajin aikin da ta shiga bayan kwana 17, inda likitocin za su ci gaba da aiki daga yau Asabar.

Shugaban ƙungiyar National Association of Resident Doctors (NARD), Dr. Emeka Orji, ya faɗa wa BBC cewa sun jingine yajin ne bayan gwamnatin tarayya ta amince da kafa gidauniyar horaswa ta Medical Residency Training Fund.

Talla

Ya ƙara da cewa gwamnatin ta fara shirin biyan su alawus na rage wahalar aikin da suke sha a asibitocin gwamnati sakamakon ficewar likitoci zuwa ƙasashen waje, kamar yadda suka nema.

A cewar Dr. Orji, waɗannan ne manya daga cikin buƙatun nasu kuma za su zauna don duba cigaban da aka samu nan da mako biyu.

Likitocin waɗanda su ne kashi 60 cikin 100 na kafatanin likitocin gwamnati a Najeriya, sun ƙaurace wa ayyuka ranar 26 ga watan Yuli, suna masu neman ƙarin kulawa da kuma inganta yanayin aikin nasu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: Bam ya fashe a Kano ya hallaka wasu ya kuma jikkata wasu

Aƙalla mutum biyar ne aka tabbatar da rasuwarsu, yayin...

Kotu a Kano ta sami wani Tela da laifin takurawa makwabtansa da karar keken dinki

Wata kotu a Kano ta samu wani tela da...

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...