Zamu Kawar da duk sharar dake Gidan Zoo na Kano – MD REMASAB

Date:

DAGA  KAMAL UMAR KURNA

Gwamnatin jihar Kano ta sha alwashin kwashe dukkanin shara tare da tsaftace gidan ajiye namun daji na Kano wato gidan Zoo.

“Wannan ziyara Babu shakka Zara Kara inganta alakar aiki tsakanin hukumarmu ta REMASAB da Gidan zoo, Kuma zamu bada duk gudunmawar da aka bukaci don Kara inganta tsaftar gidan zoo dake waje, don inganta rayuwar al’umma da dabbobin dake gidan”.

Talla

Shugaban hukumar kwashe shara da tsaftar muhalli ta jihar Kano Amb. Alhaji Ahmadu Haruna Zago ne ya bayyana hakan lokacin da shugaban hukumar gudanarwar gidan ajiye namun dajin na Kano Sadik Kura Muhammed ya kai masa ziyara domin neman taimakon hukumar kwashe sharar.

Yanzu-Yanzu: Sojojin Nijar sun Bayyana Sabon Shugaban Kasar

Dan zago yace alhakin hukumar sa ne kwashe shara a fadin birnin Kano matukar an tuntubi hukumar tasa ta hanyar data dace, a dan haka duba da yadda gidan ajiye namun dajin yake da alfanu ta hanyoyi da dama ga al’ummar Kano hukumar sa zata yi abinda ya dace cikin kankanin lokaci.

Da yake nasa jawabin tun da farko shugaban hukumar gudanarwar gidan ajiye namun dajin Sadik Kura Muhammed yace ya je ta REMASAB ne domin neman daukin hukumar, kasancewar dabbobi da al’ummar dake ziyarar gidan na namun dajin suna fuskantar matukar kalubale saboda yadda shara take neman shafe gidan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...