Majalisa ta bayyana ranar da zata fara tantance Ministoci

Date:

 

Majalisar Dattawan Najeriya ta ce a ranar Litinin ta makon gobe ne za ta fara tantance mutanen da shugaban Bola Tinubu ya tura mata domin naɗawa a matsayin ministoci.

 

Wannan dai ya zo ne bayan da ƴan ƙasar suka ƙagara su ji wadanda za su kasance ‘yan majalisar zartarwar sabon shugaban.

Talla

A ranar Alhamis Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya karanto jerin sunayen mutum 28 waɗanda shugaban ƙasar, Bola Ahmed Tinubu ya aike wa majalisar domin tantance su.

Yanzu-Yanzu: Sojojin Nijar sun Bayyana Sabon Shugaban Kasar

A tattaunawarsa da sashin Hausa na BBC, ɗan Majalisar Dattijan Najeriya, Sulaiman Kawu Sumaila, ya ce “Duk da dai ba a ƙarasa kawo sauran (sunayen) ba, amma za mu fara tantance 28 da aka gabatar a ranar Litinin mai zuwa, kuma tunda dole ne kowace jiha a samu minista, kamar yadda suka nuna shi ma sauran jerin sunayen ba da daɗewa ba za su gabatar mana da su.”

 

“Sako sunayen ƴan adawa a cikin jerin sunayen ministoci wani abu ne da zai sake samar da fahimtar juna, a yi aiki tare.” Sanata Kawu Sumaila

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...