Majalisa ta bayyana ranar da zata fara tantance Ministoci

Date:

 

Majalisar Dattawan Najeriya ta ce a ranar Litinin ta makon gobe ne za ta fara tantance mutanen da shugaban Bola Tinubu ya tura mata domin naɗawa a matsayin ministoci.

 

Wannan dai ya zo ne bayan da ƴan ƙasar suka ƙagara su ji wadanda za su kasance ‘yan majalisar zartarwar sabon shugaban.

Talla

A ranar Alhamis Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya karanto jerin sunayen mutum 28 waɗanda shugaban ƙasar, Bola Ahmed Tinubu ya aike wa majalisar domin tantance su.

Yanzu-Yanzu: Sojojin Nijar sun Bayyana Sabon Shugaban Kasar

A tattaunawarsa da sashin Hausa na BBC, ɗan Majalisar Dattijan Najeriya, Sulaiman Kawu Sumaila, ya ce “Duk da dai ba a ƙarasa kawo sauran (sunayen) ba, amma za mu fara tantance 28 da aka gabatar a ranar Litinin mai zuwa, kuma tunda dole ne kowace jiha a samu minista, kamar yadda suka nuna shi ma sauran jerin sunayen ba da daɗewa ba za su gabatar mana da su.”

 

“Sako sunayen ƴan adawa a cikin jerin sunayen ministoci wani abu ne da zai sake samar da fahimtar juna, a yi aiki tare.” Sanata Kawu Sumaila

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...