Wani lauya a Kano ya nemi yan sanda su baiwa A.A Rufa’i kariya, tare da bincikar masu tunzura shi

Date:

Daga Hafsat Lawan Sheka

 

Wani lauya mai zaman a jihar Kano wanda dake rajin kare hakkin Dan Adam Barr. Badamasi Suleiman Gandu, ya rubuta takardar korafi ga kwamishinan yan sandan jihar Kano inda ya bukaci rundunar yan sandan jihar ta binciki masu daukar bidiyon wani A. A. Rufa’I wanda yake ikirarin yafi kowa kudi a duniya.

 

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito A. A Rufa’I a kwanakin baya yayi ikirarin siyan Kano da Kaduna da Birnin Dubai da kasar Saudia da kuma wasu mayan kungiyoyin kwallon kafa kamar Real Madrid da Manchester United.

Kotu ta tabbatar da Hanga a matsayin Sanatan Kano ta tsakiya, ta kori karar APC

Majiyar Kadaura24 ta justice watch ta rawaito takarar korafin ta kuma bukaci kare hakkin AA Rufa’I da kuma lafiyar sa sakamakon yada bidiyonsa na kara kawo tasgaro a kokarin da ake na kula da lafiyar sa.

Talla

Cikin kunshin takarar korafin wacce Barr. Badamasi Gandu ya sanyawa hanu mai dauke da kwanan watan 24 ga watan Yulin, 2023 wacce kuma aka aikewa Gwamnan Kano Engr. Abba Kabir Yusuf, lauyan ya roki gwamnatin jihar Kano ta ceto A. A. Rufa’I daga halin da aka sanya shi a ciki.

Takadar Mai taken “Korafi Kan Masu Daukar Bidiyon A. A. RUFA’I” ta ce kamar yadda Allah ya Azurta Kano da Aliko Dangote da Abdussamadu Isyaka Rabi’u, haka ya Azurta ta da A. A. Rufa’I wanda yake ikirarin yafi kowa kudi a duniya sakamakon rashin lafiyar da yake fama da shi.

Lauyan ya bukaci Kwamishinan yan sandan jihar Kano da bada umarnin binciken masu dauka da kuma yada Bidiyon Mista Rufa’I domin kuma doka ta bada damar al’umma su kai rahoton duk wanda yake daukar bidiyon kuma gaza yin hakan sabawa doka ne.

Barista Badamasi Suleiman Gandu dai ya ce ya rubuta takarar korafin ne dogaro da sashi na 12 (1) na dokar kare lafiyar dan Adam na shekarar 2021 da kuma dokar kare lafiyar kowanne Dan kasa a sashi na 12 (2) (b).

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: Bam ya fashe a Kano ya hallaka wasu ya kuma jikkata wasu

Aƙalla mutum biyar ne aka tabbatar da rasuwarsu, yayin...

Kotu a Kano ta sami wani Tela da laifin takurawa makwabtansa da karar keken dinki

Wata kotu a Kano ta samu wani tela da...

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...