Tsaftar Muhalli: Zamu haɗa kai da shugabannin kasuwani a kano – Amadu Danzago

Date:

Daga Kamal Umar Kurna

 

Shugaban hukumar kwashe shara ta jihar Kano Amb. Alhaji Ahmadu Haruna Zago ya bayyana bukatar dake akwai na samar da wani tsari tsakanin hukumar sa da shugabannin kasuwannin jihar nan a bangaren tsaftace kasuwannin.

Shugaban ya bayyana hakan ne lokacin da yake tattaunawa da manema labarai a kasuwar kantin kwari, lokacin da ake gudanar da aikin kwashe sharar Wanda shine Karo na 4 a kasa da makwanni 2.

Talla

Dan zago yace hukumarsa da gwamnati ba za su cigaba da zura idanu da yawa daga cikin kasuwannin jihar nan suna cigaba da rufe tituna sanadin sharar da suke zubarwa a akan titunan ba.

Jerin sunayen ministoci: Shugaban APC, Adamu ya bayyana dalilin da ya sa Tinubu ya yi jinkiri fitar da ministoci

Wasu daga cikin ‘yan kasuwar ta kwari sun bayyana cewa ana fito da sharar ne daga cikin kasuwar a tsakiyar dare da Kuma unguwar fagge ta yadda sai dai su wayi gari suga sharar ta toshe hanyar wucewa.

Dan zago yace duba da yadda gwamnati take kashe makudan kudade wajen aikin kwashe sharar akwai bukatar al’umma su bada cikakken hadin Kai da goyon baya domin samun nasarar da aka Sanya a gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...