Dangote ya sake bada tallafi ga ‘yan Najeriya da suka dawo daga Sudan

Date:

Daga Auwalu Alhassan Kademi

 

Gidauniyar Aliko Dangote (ADF) ta bayar da tallafi ga karin ‘yan Najeriya da aka dawo da su gida Nigeria sakamakon rikicin Sudan.

 

Mutum Dari Daya da Ashirin da Biyar (125) na baya-bayan nan da suka hada da nakasassu da dama da Kamfanin Jirgin Sama na Tarco ya yi jigilar su zuwa Abuja a ranar Asabar, 24 ga watan Yuni, kowannensu ya rabauta da Naira 100,000 daga gidauniyar Aliko Dangote.

Tallah

Idan dai za a iya tunawa, sama da mutane 2,278 da suka dawo gida sun karbi Naira 100,000 kowannensu a watan Mayu, tare da kayan fakitin duk a matsayin tallafi a gare su, da kuma ba su damar haduwa da iyalansu a duk fadin kasar.

 

Gidauniyar ta sake bada tata gudunmawar ta don samun saukin dawo da ‘yan kasar da aka kwaso daga Sudan kuma daga cikinsu akwai tsofaffi, nakasassu, matasa, mata da yara.

Abba Gida-gida ya bayyana lokacin da za’a fara tura ɗalibai kasashen waje

Wasu mutane biyu ‘yan shekara 70 da suka yi niyyar tafiya tafiya ibadar umrah sun fada cikin rikicin lokacin lokacin da suka ya da zango a Khartoum, Inda kuma kuɗin su ya kara suka rasa duk abun da suka Isa kasar da shi.

‘yan Nigeria da dama ne suka yi asarar sana’o’insu daban-daban sakamakon yakin, sana’o’in da suka hada da fata, dinki, yin takalmi, saye da sayar da dai sauransu

Wani dattijo mai suna Muhammad Saidu Ahmed ya ce, “Na dawo daga Sudan ba ko kwabo ba’, yanzu ina da Naira 100,000

Tallah

Matar mai shekaru 80, ta ce yawancin iyalanta sun yi nasarar tserewa rikicin, sun shiga tashin hankali sakamakon tashin bama-bamai wanda hakan yasa suka rika fama da yunwa, sannan sun yi asarar gidajensu da wasu daga cikin yan uwansu.

Sun godewa gidauniyar Aliko Dangote, ADF, bisa wannan taimakon, wanda suka bayyana a matsayin wanda ya zo musu basu zata ba, Kuma zai taimaka musu matuka .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...