Aiki kwashe shara a manyan titunan kano zai karawa jihar kima a idon baki – Amadu Danzago

Date:

Daga Kamal Umar Kurna

Gwamnatin jihar Kano ta bayyana kwashe sharar dake jibge akan tirin gidan sarkin Kano daura da gidan Dan masani dab da Kofar shiga Makarantar SAS a matsayin Wani muhimmin aiki wanda zai Kara fito da martabar Kano.

Tallah

Shugaban kwamitin karta kwana na kwashe sharar jihar nan Alhaji Ahmadu Haruna zago, shi ne ya bayyana hakan a daren yau lokacin da jami’an hukumar kwashe shara ta jihar nan suka yi dirar mikiya a wajen domin gabatar da ayyukansu.

 

A cewar Dan zago hanyar zuwa gidan Dan masani da Kofar shiga Makarantar S.A.S, wurare ne masu matukar muhimmanci da tarihi ga al’ummar jihar nan, a don haka akwai bukatar Samar da kyakkyawan yanayi a wuraren domin samun cikakkiyar tsafta.

Ganduje ya Magantu kan dakatar da albashin ma’aikata dubu 10 da gwamnatin Kano ta yi

” Wannan kwamiti na mu yana aiki ba dare ba rana ne don mu tsaftace jihar kano da kuma magance cututtuka da shara take haifarwa, sanann kuma yin hakan zai kara fito da martabar jihar a idon bakin dake shigowa Kano kowacce Rana”. Inji shi

Dan zago daga nan sai ya bukaci al’ummar dake rayuwa a yankunan dasu kasance masu bin doka da oda ta hanyar kai sharar su wuraren da hukuma ta tanada domin zubarwa domin samarwa da kansu ingantacciyar rayuwa me cike da lafiya da tsafta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...