Emefiele ya maka gwamnatin tarayya a Kotu

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnan Babban Bankin Najeriya da aka dakatar, Mista Godwin Emefiele ya shigar da ƙara a gaban wata babbar kotun tarayya, yana ƙalubalantar tsare shi da hukumar tsaron farin kaya ta DSS ke yi.

 

A cikin ƙudurin da ya gabatar, Emefiele ya nemi kotu ta tilasta wa hukumomi tabbatar masa da ‘yancinsa na walwala da ‘yancin zirga-zirga, don kuwa a cewarsa, babu hujjar ci gaba da tsare shi.

Da dumi-dumi: Shekarau ya Magantu kan gayyatar da Majalisar Dinkin duniya ta yi masa

Sai dai, Ofishin Atoni Janar na Tarayya da kuma hukumar DSS sun ce tsare dakataccen gwamnan bankin yana kan doka.

 

Sun kuma ce tsare jami’in ya dogara ne kan wani umarnin kotun majistare don haka suka nemi babbar kotun ta kori buƙatar da Emefiele ya gabatar.

Da dumi-dumi: Abba Gida-gida ya Magantu kan baiwa dansa mukami

Sun nunar da cewa kama tsohon gwamnan babban bankin na Najeriya yana kan tsarin gudanarwa na hukumar ta DSS.

Yayin da Atoni Janar na Tarayya ya ƙalubalanci hurumin kotun na sauraron ƙarar, saboda ƙudurin da Godwin Emefiele ya gabatar na neman kotu ta jingine umarnin tsare shi ne, maimakon neman a tabbatar masa da ‘yancinsa.

Haka zalika, ita ma hukumar DSS a nata ɓangare ta ƙalubalanci ƙudurin neman beli da Mista Emefiele ya gabatar.

 

Tallah

BBC ta rawaito daga bisani, kotu ta ɗage shari’ar zuwa ranar 13 ga watan Yuli don yin hukunci kan wannan buƙata.

A ranar 10 ga watan Yuni ne Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya dakatar da Godwin Emefiele daga matsayin Gwamnan Babban Bankin ƙasar, daga bisani kuma hukumar DSS ta sanar da cewa tana tsare da shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...