Majalisar dokokin jihar kano ta bayyana ranar da zata fara tantance kwamishinoni

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Majalisar dokokin jihar kano ta ce zata fara tantance sabbin wadanda gwamnan kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya tura musu mata sunayen su a ranar Laraba 21 ga watan Yuni 2023.

 

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito gwamnan Abba Kabir Yusuf ya tura sunayen mutane 19 wadanda ya buƙaci majalisar ta tantance su domin ya nada su a matsayin kwamishinoninsa.

Yanzu-Yanzu: Abba Gida-gida ya tura sunayen wadanda zai nada a matsayin kwamishinoni

Shugaban majalisar Hon. Jibril Falgore ne dai ya karata wasikar da gwamnan ya turawa Majalisar Mai dauke da sunayen.

Tallah

Da suke bada gudunmawa yayin zaman majalisar na wannan rana, dan majalisar mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado/ Tofa, Muhammad Bello Butu-Butu da na karamar hukumar Ungoggo Aminu Sa’adu Ungoggo, sun bayyana cewa tantance sabbin kwamishinonin da wurin zai taimaka ciyar da jihar kano gaba.

Yanzu-Yanzu: Tinubu ya rushe majalisun gudanarwar Hukumomi, ma’aikatu da kamfanonin gwamnatin tarayya

Suka ce tantancewa da Amincewa da sunayen da akan lokaci zai baiwa ɓangaren zartarwa damar rantsar da su akan kari domin fara aikin su don ciyar da jihar kano gaba ta konne ɓangare.

Kwamishinoni sune yan majalisar zartarwa Kuma suna bada gudunmawa ga ɓangaren zartarwa wajen aiwatar da manufofi da kudirorin gwamnati kamar yadda kundin tsarin mulki Nigeria ya tanada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...