Majalisar dokokin jihar kano ta bayyana ranar da zata fara tantance kwamishinoni

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Majalisar dokokin jihar kano ta ce zata fara tantance sabbin wadanda gwamnan kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya tura musu mata sunayen su a ranar Laraba 21 ga watan Yuni 2023.

 

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito gwamnan Abba Kabir Yusuf ya tura sunayen mutane 19 wadanda ya buƙaci majalisar ta tantance su domin ya nada su a matsayin kwamishinoninsa.

Yanzu-Yanzu: Abba Gida-gida ya tura sunayen wadanda zai nada a matsayin kwamishinoni

Shugaban majalisar Hon. Jibril Falgore ne dai ya karata wasikar da gwamnan ya turawa Majalisar Mai dauke da sunayen.

Tallah

Da suke bada gudunmawa yayin zaman majalisar na wannan rana, dan majalisar mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado/ Tofa, Muhammad Bello Butu-Butu da na karamar hukumar Ungoggo Aminu Sa’adu Ungoggo, sun bayyana cewa tantance sabbin kwamishinonin da wurin zai taimaka ciyar da jihar kano gaba.

Yanzu-Yanzu: Tinubu ya rushe majalisun gudanarwar Hukumomi, ma’aikatu da kamfanonin gwamnatin tarayya

Suka ce tantancewa da Amincewa da sunayen da akan lokaci zai baiwa ɓangaren zartarwa damar rantsar da su akan kari domin fara aikin su don ciyar da jihar kano gaba ta konne ɓangare.

Kwamishinoni sune yan majalisar zartarwa Kuma suna bada gudunmawa ga ɓangaren zartarwa wajen aiwatar da manufofi da kudirorin gwamnati kamar yadda kundin tsarin mulki Nigeria ya tanada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...