Janye tallafin mai: Ƙungiyar ‘Yan jarida a Najeriya za ta fara yajin aiki

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya NUJ ta ce za ta bi sahun ƙungiyar Kwadago wajen tsunduma yajin aiki daga ranar Laraba mai zuwa, saboda cire tallafin man fertur a Nigeria.

KAYYASA: Kalli yadda Gwamnan Kano Abba Gida-gida ya fara rushe gine-gine (hotuna)

Ƙungiyar ta bayyana hakan ne a cikin wata takarda da ta fitar, bayan ganawar da kwamtin gudanarwarta ya yi da safiyar ranar Asabar domin tattauna batun cire tallafin man fetur da gwamnatin ƙasar ta yi da kuma matakin ƙungiyar ƙwadago ta NLC ta ɗauka na shiga yajin aiki a tsakiyar makon da ke tafe.

Ƙungiyar ta NUJ ta ce a halin da ake ciki tashin farashin man fetur da na sauran kayayyaki sun jefa al’ummar ƙasar cikin mawuyacin hali.

Haka kuma ƙungiyar ta umarci mambobinta da ke faɗin jihohin ƙasar da su fara yajin aiki tare da fita zanga-zanga daga ranar Laraba 7 ga watan Yuni matuƙar kamfanin mai na ƙasar NNPCL bai janye ƙarin farashin man fetur da ya yi ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...