Janye tallafin mai: Kungiyar ƙwadago za ta fara yajin aiki a mako mai zuwa

Date:

Daga Rahma Umar Kwaru

 Kungiyar kwadago ta Najeriya NLC ta bayyana cewa za ta shiga yajin aikin gama gari daga ranar Laraba mai zuwa.
 Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake fama da tsadar mai a fadin kasar sakamakon jawabin da shugaban kasa Bola Tinubu ya yi na kaddamar da shi inda ya bayyana cewa ” tallafin man fetur ya kare”.
 Shugaban kungiyar ta NLC, Joe Ajaero ne ya bayyana hakan bayan wani taron gaggawa na majalisar zartarwar kungiyar ta kasa a Abuja.
 Ya ce gwamnati, musamman ma kamfanin man fetur na kasa (NNPC) da ya dawo da tsohon farashin man zuwa ranar Larabar mako mai zuwa in kuma ba haka ba zasu kirawo yajin aiki a duk fadin kasa.
 Ajaero ya kara da cewa rashin cika wa’adin da gwamnatin tarayya ta yi zai janyo zanga-zangar da ba a taba yin irin ta ba a fadin kasar nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...