Kungiyar yan Jaridu ta ARTV ta karrama Hadimin Ganduje Aminu Dahiru

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Kungiyar yan jaridu ta kasa reshen gidan Talabishin na Abubakar Rimi wato (NUJ ARTV Chapel) ta karrama mataimaki na musamman ga Gwamnan jihar kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje a fannin hoto, Aminu Dahiru Ahmad da lambar yabo.

 

Da yake mika lambar yabon ga Aminu Dahiru Shugaban kungiyar Kwamared Abubakar Shehu kwaru yace sun karrama mataimaki na musamman ga gwamnan ne bisa irin gudunmawar da yake baiwa matasa da kuma kungiyar.

Ku gina al’umma maimakon ku rika sace dukiyoyinsu – Kwankwaso ya fadawa ‘yan siyasa

“Mun baiwa Aminu Dahiru Ahmad wannan lambar yabo ne saboda gagarumar gudunmawar da ya ke bayarwa wajen bunkasa reshen Kungiyar mu da kuma aikin jarida a jihar Kano baki daya”. Inji Abubakar Kwaru

Hadimin Ganduje Aminu Dahiru ya baiwa wasu matasa tallafin karatu a Kano

Yace a lokuta da dama Aminu Dahiru ya kan taimakawa matasa don su dogara da kawunansu, sannan kuma yana taimakawa kungiyar irin na mu don su sami damar inganta walwalar mambobinsu .

Jim kadan bayan karbar lambar yabon Aminu Dahiru Ahmad ya godewa kungiyar bisa karramawar da suka yi masa, sannan yace hakan zai taimaka wajen karamasa kwarin gwiwar cigaba da taimakawa kungiyoyi.

” Ni matashi ne bani da wani dalili da bazan taimakawa matasa yan uwana matasa ba, shi matashi idan ka taimake shi ba shi kadai ka taimaka ba don haka muke amfani da damar da Allah ya bamu wajen taimakawa matasa daidai gwargwado.

Aminu Dahiru ya kuma bukaci kungiyoyi da su rika mai da hankali wajen samar da walwala ga mambobinsu, domin hakan shi ne ribar kungiya da Kuma taimakawa juna.

Aminu Dahiru dai ya sami lambobin yabo daga kungiyoyi daban-daban bisa yadda yake taimakawa wajen cigaba da inganta rayuwar matasa ta fannoni daban-daban

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...