Kotu ta haɗe shari’ar zaɓen shugaban kasa waje ɗaya

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Kotun da ke sauraren shari’ar zaben shugaban kasa ta Najeriya ta hade kararraki guda uku da ‘yan hamayya suka shigar gabanta a kan sakamakon zaben ranar 25 ga watan Fabarairu wanda hukumar zabe INEC ta bayyana Bola Ahmad Tinubu na APC a matsayin wanda ya lashe zaben.

 

A rahoton da kotun mai alkalai biyar ta fitar wanda jagoranta Justice Haruna Tsammani ya karanta yau Talata, ta kotun ta umarci fara sauran korafin su Peter obi da jam’iyyarsa ta Labour a ranar 30 ga watan Mayun nan.

Wadanda suka shigar da kararrakin su ne dan takarar shugaban kasa na PDP Atiku Abubakar da jam’iyyar, sai Peter Obi tare da jam’iyyarsa ta Labour, sai kuma jam’iyyar Allied Peoples Movement (APM).

Kotun ta umarci masu karar da su gabatar da korafe-korafensu a cikin mako uku wanda cikin lokacin za ta kirawo masu gabatar da shedar da aka ware guda 50, daga ranar 30 ga watan na Mayu a lokacin da za masu korafin za su fara kiran masu sheda a kuma kammala a ranar 23 ga watan Yuni.

Kotun ta ce za a kammala shari’ar a ranar 5 ga watan Agusta a lokacin da lauyoyn masu karar za su gabatar da jawabansu na karshe a rubuce, daga nan kuma kotun za ta ware ranar da za ta bayyana hukuncinta

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...