Akwai yiwuwar za’a jima ba a shawo kan rikicin Sudan ba – MDD

Date:

 

Babban jami’in ba da agaji na Majalisar Ɗinkin Duniya , ya bayyana cewa zai yi wuya a kawo karshen faɗan da ake gwabzawa a Ƙasar Sudan, saboda ɓangarorin da ke rikici da juna ba su nuna yunkurin hakan ba.

Ya ce akwai damuwa matuka na yadda rikicin ke ci gaba da yaɗuwa.

 

Martin Griffiths yana magana ne da BBC bayan ya ziyarci Port Sudan da ke gaɓar tekun Bahar Maliya.

Da dumi-dumi: Allah kadai yasan jam’iyyar da zan mikawa mulkin Kano – Ganduje

“Kuma duk wata hanya ta samar da tsagaita wuta a ƙasar ya citura saboda ɓangarorin sun ki amincewa da hakan,” in ji Martin

Ranar Yan Jaridu: Zan baiwa yan jaridu damar gudanar da aikin su ba tare da tsangwama ba – Abba Gida-gida

Ya ce ya kirayi janar-janar ɗin da ke faɗa da juna da su zauna teburin sulhu wajen ganin an kai kayan agaji cikin gaggawa da kuma shawo kan rikicin.

Ya ce ɓangarorin biyu da ke gaba da juna sun yi magana game da ra’ayinsu kan ka’idojin jin kai – amma da alama ba a yi niyyar kawo karshen yakin ba.

Ana shirin soma wani sabon tsagaita wuta na kwanaki bakwai – amma tsagaita wuta da aka cimma a baya ta ruguje.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...