Akwai yiwuwar za’a jima ba a shawo kan rikicin Sudan ba – MDD

Date:

 

Babban jami’in ba da agaji na Majalisar Ɗinkin Duniya , ya bayyana cewa zai yi wuya a kawo karshen faɗan da ake gwabzawa a Ƙasar Sudan, saboda ɓangarorin da ke rikici da juna ba su nuna yunkurin hakan ba.

Ya ce akwai damuwa matuka na yadda rikicin ke ci gaba da yaɗuwa.

 

Martin Griffiths yana magana ne da BBC bayan ya ziyarci Port Sudan da ke gaɓar tekun Bahar Maliya.

Da dumi-dumi: Allah kadai yasan jam’iyyar da zan mikawa mulkin Kano – Ganduje

“Kuma duk wata hanya ta samar da tsagaita wuta a ƙasar ya citura saboda ɓangarorin sun ki amincewa da hakan,” in ji Martin

Ranar Yan Jaridu: Zan baiwa yan jaridu damar gudanar da aikin su ba tare da tsangwama ba – Abba Gida-gida

Ya ce ya kirayi janar-janar ɗin da ke faɗa da juna da su zauna teburin sulhu wajen ganin an kai kayan agaji cikin gaggawa da kuma shawo kan rikicin.

Ya ce ɓangarorin biyu da ke gaba da juna sun yi magana game da ra’ayinsu kan ka’idojin jin kai – amma da alama ba a yi niyyar kawo karshen yakin ba.

Ana shirin soma wani sabon tsagaita wuta na kwanaki bakwai – amma tsagaita wuta da aka cimma a baya ta ruguje.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...