Da dumi-dumi: Alhassan Ado Doguwa ya bayyana aniyarsa ta neman Shugabancin majalisar wakilai

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Doguwa da Tudun Wada Hon. Alhassan Ado Doguwa ya bayyana bukatarsa ta tsayawa neman takarar shugaban majalisar wakilai ta goma da za’a kafa.

” Ina neman hadin kanku don ku sahalle min na zama Shugaban majalisar wakilai ta 10 don ciyar da kasar nan gaba, da kuma inganta aiyukan majalisa da kuma samar da cigaban ta kowacce fuska a Nigeria”.

Da dumi-dumi: Kwankwaso ya Magantu a kan batun dawo da Sarki Sunusi II Sarautar Kano

Kadaura24 ta rawaito cikin wata wasika da Alhassan Ado Doguwa ya aikewa abokanan aikin sa yan majalisar, ya nemi hadin kan yan majalisar don zama Shugaban su.

 

” Ina taya ku murnar lashe zabukan ku wanda hakan ya baku damar kasancewa wannan majalisar, Ina so ku ajiye banbancin addini, kabilanci, bangaranci da kuma jam’iyyar siyasa ku bani dama don na zama Shugaban majalisa ta goma don cigaban Nigeria”. Inji Doguwa

 

Yanzu haka dai hankalin al’ummar Nigeria musamman ‘yan siyasa ya koma kan ganin waye zai zama Shugaban majalisa wakilai da kuma majalisar dattawa ta kasa.

 

Yan majalisu da dama dai sun fito don neman wadannan mukamai, sai dai zaɓaɓɓen shugaban ƙasa Bola Tinubu da jam’iyyar APC na kokarin ganin an sami shugabannin ba tare da yan shiga zabe ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...