Shugabancin majalisa: Abubuwan da aka tattauna tsakanin Tinubu, Akpabio da Barau Jibri

Date:

Daga Safiyanu Dantala Jobawa

 

Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya kammala shirin naɗa tsohon gwamnan Akwa Ibom, Sanata Godswill Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa, da kuma Sanata Barau Jibrin a matsayin mataimakin sa.

Sahihan majiyoyi sun bayyana wa jaridar Daily Trust cewa tuni Tinubu ya sanar da Akpabio da Barau wannan ƙuduri nasa a wata ganawar sirri da su ka yi a Abuja bayan dawowarsa daga ƙasar Faransa.

Yakin Sudan: Rukunin farkon na daliban Najeriya sun Isa Ƙasar Masar – Gwamnatin tarayya

Kadaura24 ta rawaito cewa Akpabio da Barau na cikin ƴan takara 9 da ke neman shugabancin majalisar dattawa, wanda za a rantsar da su a ranar 13 ga watan Yuni.

 

Majiyoyin sun tabbatar wa da Daily Trust cewa a yayin ganawar, wacce dama sabo da Barau a ka yi ta, Tinubu ya rarrashe shi da ya hakura da takarar shugabancin majalisar dattawa domin a samu adalci da daidaito na addini a shugabancin ƙasar.

Yanzu Yanzu: Shugaba Buhari ya halarci Faretin Sojoji Sanye da kakin Soji

A cewar majiyoyin, Tinubu ya nunawa Barau cewa ya cancanta da ya zama shugaban majalisar dattawa, to amma kasancewar Tinubu da mataimakin sa Kasim Shettima musulmai ne, ya kamata a ce Barau ya ajiye burin nasa ya baiwa kirista dan kudu dama domin a samu daidaito da kuma zaman lafiya a mulkin ƙasar.

“A ƙarshen ganawar ne sai Tinubu ya shaidawa Barau cewa yana don ya zama mataimaki ga Akpabio su yi aiki tare,” in ji majiyoyin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...