Abubuwan da dokar majalisar masarautun jihar kano ta kunsa

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Majalisar dokokin jihar Kano ta yi wa dokar majalisar masarautun jihar Kano gyare-gyare .

 

Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar kiru Hon. Kabiru Hassan Dashi wanda kuma shi ne mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar ta Kano ya shaida wa BBC abinda sabbin dokokin suka ƙunsa.

 

Kabiru Dashi ya ce dokokin guda biyu ne, ɗaya gyara aka yi mata, yayin da ɗayar kuma sabuwa ce.

 

Rashin wuta: ‘Yan KEDCO ya kamata ku nemi aljannar ku a wanann wata na Ramada – Falakin Shinkafi

Ya ce dokar da aka yi wa gyaran ita ce dokar majalisar masarautun jihar, inda dokar ta tanadi rage adadin mambobin majalisar masarautar daga 30 zuwa 17.

 

Sannan kuma ya ce daga cikin gyare-gyaren dokar, daga yanzu kwamishinan ‘yan sandan jihar da shugaban hukumar DSS na jihar da shugaban hukumar tsaro ta Civil Defence, da kuma shugaban ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin jihar, duk suna cikin mambobin majalisar masarautun jihar.

Zaɓen Gwamnan Kano: APC ta roki kotun sauraren kararrakin Zabe har abubuwa guda 5

 

A gefe guda kuma Hon. Kabiru ya ce an samar da sabuwar doka kan masarautun Gaya da Ƙaraye da kuma Rano, inda a yanzu sabuwar dokar ta tanadi cewa dole sai ‘yan asalin gidan masarautun ne kawai za su yi sarauta a masarautun.

 

”Kamar dai yadda yake a masarautun Kano da Bichi inda doka ta tanadi cewa dole sai ‘yan gidan Dabo ne kawai za su yi mulki a masarautun”, in ji shi.

 

Dan majalisar ya ce su ma masarautun Gaya da Ƙaraye da Gaya an zaƙulo wasu mutane waɗanda tun asali su ne suke mulki a masarautun.

 

”Yanzu misali kamar gidan sarki Gaya akwai gidan Abubakar Sayyadi, gidan sarautar Rano kuma akwai sarki Ila, gidan Karaye kuma akwai gidan sarki Alu”, in ji shi

A cewarsa waɗannan su ne gidajen da dokar ta ce dole sai waɗanda suka fito daga tsatson gidajen ne kawai za su riƙe sarautar masautun.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

A Gaggauce: Fadar shugaban Kasa ta musanta murabus din Sakataren gwamnatin tarayya

Daga Rahama Umar Kwaru Fadar shugaban Kasa ta musanta labarin...

Gawuna ya mika ta’aziyyar rasuwar Alhaji Aminu Dantata

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna...

Nijeriya ta yi babban rashi: Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Aminu Dantata

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya...

Rasuwar Alhaji Aminu Dantata ta bar gibin da zai yi wuyar cikewa a Nigeria – Alhaji. Kabiru Sani Kwangila

Shugaban kamfanin gine-gine na SKY Alhaji Kabiru Sani Kwangila...