Ramadan: Mutune sama da miliyan 1 ne suka je Ibadar Umara Saudiyya

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

Ministan ma’aikatar aikin Hajji da Umara ta ƙasar saudiyya Dr. Tawfiq Al-Rabiah ya bayyana cewa biranen Makka da Madina sun samu masu ziyarar ibada daga ƙasashen waje masu yawan gaske a wannan wata.

 

Dr. Tawfiq ya ce ya zuwa yanzu an samu masu ziyarar ibada miliyan 1.3 a manyan biranen ƙasar biyu.

 

Likitoci a Najeriya sun soki sabon ƙudurin Majalisar wakila ta ƙasa

Ministan ya ce ana samun ci gaba a harkokin sufurin masu ziyarar ibada tare da inganta harkokin ibada musamman a cikin masallatai biyu masu alfarma a ƙasar.

Yan mata sama da dubu 42 ne suka daina zuwa makaranta saboda sun yin ciki – Rahoto

 

”Muna bakin ƙoƙarinmu wajen samar da kyakkyawan yanayi domin jin daɗin mahajjata a biranen Makka da Madina”, in ji shi.

 

”A kodayaushe muna kan inganta biranen biyu, kuma akwai wuraren tarihi sama da 100 tsakanin biranen biyu”, a cewarsa.

 

Ministan ya ce ana sa ran sama da mutune miliyan biyu ne za su yi aikin hajjin bana a wannan shekara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...