Daga Maryam Muhammad Ibrahim
Hukumar Jin dadin alhazai ta jihar kano tace dalilai ne Masu yawa suka sa kudin kujerar aikin hajjin bana ta yi tashin gwaron zabi a Nigeria da duniya baki daya.
Sakataren zartarwa na hukumar Malam Muhammad Abba Danbatta ne ya bayyana hakan Yayin da ya gana da manema labarai bayan Jim kadan bayan Nahcon ta sanar da kudin aikin hajjin bana.
Danbatta yace tashin da dalar Amurka ta yi na daya daga cikin dalilin tashin kudin, sai Kuma batu sake ginin masaukan alhazai a kasa mai tsarki da hukumomin kasar sake yi, don inganta Jin dadi da walwalar alhazai bakin Allah.
Kammala zaben 2023: Abba Gida-gida ya baiwa shugabannin kananan hukumomin Kano shawara
” Akwai Kuma batun tashin fara shin dajunkunan da alhazai suke amfani da su manya da kanana dukkanin su farashin su ya tashi ba kamar yadda suke a bara ba, shi ma uniform da ake baiwa alhazai ya tashi Inda a baya muke basu kala biyu akan Naira dubu 6, Amma a bana zai tashi ne akan naira dubu 8, sannan shi kansa tikitin jirgin sama ya tashi saboda tsadar man jirgi da dai sauransu”. Inji Muhd Abba Danbatta
Alhassan Ado Doguwa ya yi Nasara, Kotu ta bada umarnin karasa zaben Tudun Wada da Doguwa
Sakataren zartarwar ya kuma ce maniyata aikin hajjin bana zasu biya kuɗin kujera Naira Miliyan 2 da dubu dari tara da goma Sha tara, Inda yayi kira ga duk wadanda basu cika kudin ba da su hanzarta cikawa kafin ranar 21 ga wannan wata na afirilu domin ita ce ranar da za’a rufe karbar kuɗin kujerar aikin hajji a kasa baki daya.