Malam Bashir ya kafa wa Abduljabbar hujja cewa babu wani lafazi da ya alakanta da “kawaliya”
Ya ce: “Annabi Ya tura Ummusulaimin ga wata budurwa da ta duba masa bakinta da digadiginta, ba da manufar da shi Malam Abduljabbar ya ambata ba. Yace al’aurar mace zuwa ga mace ba ya zama al’aura kamar yada yake ga namiji zuwa namiji.
Malamin ya kuma zargi Abduljabbar da cewar maganar ridda suna sane da ita, amma sai gashi a kwanakin baya, an jiyo shi ya ce mutum milliyan biyu sun yi ridda aMasar

Sannan ya ba shi amsar cewar bai je Masar din da yake da’awar zuwa ba Sudan ya je
Sannan mutumin da yake da’awar cewar yana yada farfaganda an kure shi, sai dai ya ce yana fadar hadisan da babu su.
Sannan akwai hadisan da yake fada da ba zai same su ba, domin da tuni malaman da suka gabata sun fito da su.
Malam Bashir ya ce dukkanin abin da suke fada shi Mallam Abduljabbar ne ya fada
Ya yi kira ga Abduljabbar da ya tuba, ya janye kalamansa.
Da aka ba Abduljabbar damar ya bayar da amsa sai ya nuna cewa har yanzu yana kan kalamansa na farko cewar minti goma ya yi kadan.
Kuma ya gaza bayar da amsar cewar a ina annabi SAW ya ke aika UmmuSulaim na zuwa ta gano masa tsiraicin mata.
Malam Bashir Ya ja hankalin Mallam Abduljabbar cewar da ya daure ya ringa fadar litattafan da yake da’awar a inda hadisan suke amma ya gaza
Ya ƙara jan hankalinsa da cewar dukkan abin da mutum ya fada abin tambaya ce ranar gobe kiyama
Allah yasa mu dace ameen
ai ita qarya fure takeyi bata ya’ya mabiyan wannan aqida da kuma malamin ya rage naku. wlh ku gaggauta tuba wurin mahalicin ku tun kafin lokaci ya qure