Tinubu ya tafi Hutu London, Paris ya kuma wuce Saudiyya

Date:

Sabon zaɓaɓɓen shugaban Najeriya Bola Tinubu ya tafi Turai domin ya hutu, daga can kuma zai nufi Saudiyya domin aikin Umrah.

 

Kakakin Tinubun Tunde Rahman ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a yau Laraba.

 

A sanarwar kakakin ya ce, Tinubun ya fita ne domin ya je ya huta daga gajiyar kakar yakin neman zabe da kuma zaben sannan kuma ya tsara shirinsa na karbar mulki kafin ranar kaddamarwarsa ta 29 ga watan Mayu na shekarar nan ta 2023.

 

Tunde ya ce zaɓaɓɓen shugaban ya tashi daga filin jirgin sama na Murtala Mohammed da ke Ikeja, a Lagos zuwa Turai a jiya Talata da daddare, inda zai je Paris da kuma London domin ya huta, sannan kuma ya wuce Saudiyya domin Umrah da azumin Ramadan da za a fara a gobe Alhamis.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...