Tinubu ya tafi Hutu London, Paris ya kuma wuce Saudiyya

Date:

Sabon zaɓaɓɓen shugaban Najeriya Bola Tinubu ya tafi Turai domin ya hutu, daga can kuma zai nufi Saudiyya domin aikin Umrah.

 

Kakakin Tinubun Tunde Rahman ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a yau Laraba.

 

A sanarwar kakakin ya ce, Tinubun ya fita ne domin ya je ya huta daga gajiyar kakar yakin neman zabe da kuma zaben sannan kuma ya tsara shirinsa na karbar mulki kafin ranar kaddamarwarsa ta 29 ga watan Mayu na shekarar nan ta 2023.

 

Tunde ya ce zaɓaɓɓen shugaban ya tashi daga filin jirgin sama na Murtala Mohammed da ke Ikeja, a Lagos zuwa Turai a jiya Talata da daddare, inda zai je Paris da kuma London domin ya huta, sannan kuma ya wuce Saudiyya domin Umrah da azumin Ramadan da za a fara a gobe Alhamis.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...