2023: Obasanjo ya bukaci a soke zaɓen shugaban ƙasa

Date:

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya ce zaben shugaban kasa da aka yi a ranar Asabar bashi da inganci don haka akwai bukatar dole soke shi.

 Obasanjo ya roki shugaban hukumar zabe mai zaman kanta Farfesa Mahmood Yakubu da ya ceci Najeriya daga cikin hadarin da take neman fadawa .
A cikin sanarwar da Obasanjo ya fitar ya ce ba wani boyayyen abu ba ne yadda jami’an INEC a rumfunan zabe sun gaza yin amfani da na’urar da aka tanadar musu, wanda hakan tasa ake zargin sun yi aringizon kuri’u.
 Idan dai za a iya tunawa, a ranar 1 ga watan Janairu, Obasanjo ya fito fili ya amince zai goyi bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi, a wannan zaben da aka gudanar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Adam A Zango ya sake Aurar Jarumar Kannywood

Fitaccen jarumin masana’antar shirya fina-finan Hausa, Kannywood, Adam A....

NNPP ta yi watsi da sakamakon Zaben Ghari da Tsanyawa a Kano

Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano ta ƙi amincewa da...

Kwankwaso ya yi tsokaci game da zaben cike gurbi da akai a Kano

Jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana...

A Hukuma ce INEC ta bayyana sakamakon zabukan cike gurbi da aka yi a kano

Hukumar zabe mai zamanta ta Kasa ta bayyana Dan...