A Hukuma ce INEC ta bayyana sakamakon zabukan cike gurbi da aka yi a kano

Date:

Hukumar zabe mai zamanta ta Kasa ta bayyana Dan takarar Jam’iyyar NNPP Ali Lawan Alhassan a matsayin wanda ya lashe zaben cike gurbi na dan majalisar Jiha na kananan hukumomin Bagwai da Shanono da kuri’u 16,198.
yayin da dantakarar APC ya samu kuri’u 5,347.

Baturen zaɓen Farfesa Hassan Adamu Shitu ne ya sanar da sakamakon da misalin ƙarfe 12:36am.

FB IMG 1753738820016
Talla

Haka zalika hukumar zaben ta bayyana Dan takarar Jam’iyyar APC Garba Yau Gwarmai a matsayin wanda ya lashe zaben Dan Majalisar jiha mai wakiltar kananan hukumomin Ghari da Tsanyawa a Majalisar dokokin jihar Kano .

Baturen zaɓen yankin, Farfesa Muhammad Waziri, ne ya sanar da sakamakon zaben da ƙarfe 6:10 na safiyar wannan Lahadi.

Farfesa Waziri ya ce jam’iyyar APC ta samu kuri’u 31,472, yayin da NNPP ta sami kuri’u 27,931.

Adan haka ya ce Garba Ya’u Gwarmai, na jam’iyyar APC ne ya lashe zaɓen cike gurbin na mazaɓar Ghari da Tsanyawa a majalisar dokokin jihar Kano, da aka gudanar a jiya Asabar .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...