Zaben Shugaban Kasa: Kwankwaso ya doke Tinubu da Atiku a Kano

Date:

Daga Yakubu Abubakar Gwagwarwa

 

 

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta bayyana cewa Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ne ya Sami kuri’u mafi rinjaye a zaben Shugaban kasa da aka gudanar a jihar Kano.

 

Babban jami’in tattara sakamakon zabe Shugaban kasa a Kano Farfesa Lawan Sulaiman Bilbis ne ya bayyana hakan Jim kadan bayan karbar sakamakon Zaɓen daga kananan hukumomin 44 dake jihar kano.

 

Farfesa Bilbis yace Kwankwaso ya Sami kuri’u 997279 yayin da abokin takarar sa na jam’iyyar APC Asiwaju Bola Ahmad Tinubu ya zo na biyu da kuri’u 517341sai Kuma Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP na ya ke biye masa da kuri’u 131716.

 

Babban jami’in tattara sakamakon Zaɓen ya bayyana sakamakon Zaɓen Shugaban kasa na kano ne a gaban wakilan jam’iyyu da masu Sanya idanu na gida dana waje da jami’an tsaro da kuma yan jaridu.

 

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito an gudanar da zaben Shugaban kasa dana yan majalisun tarayya a ranar asabar 25 ga watan fabarairun 2023.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...