Tarukan Siyasa: Rundunar Yan Sanda Kano ta baiwa jam’iyyun APC NNPP da PDP Shawara

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

Rundunar yan sanda ta kasa reshen jihar Kano ta gana da wakilan jam’iyyun APC NNPP da PDP domin a shawo kansu game da yakin neman zabe da jam’iyyun suka shirya gudanarwa yau Alhamis a Kano.
Kadaura24 ta rawaito Kwamishinan yan sanda na jihar kano CP Muhammad Yakubu ne ya jagoranci Zaman wanda aka yi shi da zummar sanar da su illar da yin tarukan nasu a rana guda zai haifar da Kuma yiyuwar samun matsala ga Zaman lafiya da ake da shi a Kano.
Talla
Jami’in hulda da jama’a na rundunar yan sandan kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a safiyar yau Alhamis.
Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil
” Bayan samun labarin dukkanin wannan jam’iyyu guda uku suna son gudanar da tarukan yaƙin neman zabe a yau Alhamis, hakan tasa kwamishinan ‘yan sandan jihar kano CP Muhammad Yakubu ya gayyato wakilan jam’iyyun donin samun masalaha , Amma daga karshe dai masalahar bata Samu ba”. Inji
Kiyawa ya ce kwamishinan ya baiwa jam’iyyun shawarar dukkanin su su hakuri da yin taron, su bari sai bayan zaben Shugaban Kasa wanda za’a yi ranar Asabar Mai zuwa saboda kusancin da wuraren taron ke da shi ga na wata jam’iyyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...