Tarukan Siyasa: Rundunar Yan Sanda Kano ta baiwa jam’iyyun APC NNPP da PDP Shawara

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

Rundunar yan sanda ta kasa reshen jihar Kano ta gana da wakilan jam’iyyun APC NNPP da PDP domin a shawo kansu game da yakin neman zabe da jam’iyyun suka shirya gudanarwa yau Alhamis a Kano.
Kadaura24 ta rawaito Kwamishinan yan sanda na jihar kano CP Muhammad Yakubu ne ya jagoranci Zaman wanda aka yi shi da zummar sanar da su illar da yin tarukan nasu a rana guda zai haifar da Kuma yiyuwar samun matsala ga Zaman lafiya da ake da shi a Kano.
Talla
Jami’in hulda da jama’a na rundunar yan sandan kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a safiyar yau Alhamis.
Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil
” Bayan samun labarin dukkanin wannan jam’iyyu guda uku suna son gudanar da tarukan yaƙin neman zabe a yau Alhamis, hakan tasa kwamishinan ‘yan sandan jihar kano CP Muhammad Yakubu ya gayyato wakilan jam’iyyun donin samun masalaha , Amma daga karshe dai masalahar bata Samu ba”. Inji
Kiyawa ya ce kwamishinan ya baiwa jam’iyyun shawarar dukkanin su su hakuri da yin taron, su bari sai bayan zaben Shugaban Kasa wanda za’a yi ranar Asabar Mai zuwa saboda kusancin da wuraren taron ke da shi ga na wata jam’iyyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...