An cire Naja’atu Muhammad daga aikin sanya ido kan ‘yan sanda lokacin zaɓe

Date:

 

Hukumar lura da aikin ‘yan sanda ta Najeriya ta maye gurbin Hajiya Naja’atu Mohammed, a matsayin ɗaya daga cikin masu sanya idanu na hukumar da za su lura da ayyukan ‘yan sanda a yankin arewa maso yammacin ƙasar a lokacin babban zaɓen ƙasar da ke tafe.

 

A wata sanarwa da hukumar ta fitar ta ce an janyo hankalinta ne kan wata sanarwa da jam’iyyar APC mai mulki ta fitar, inda ta yi zargin cewa Hajiya Naja’atu na goyon bayan wata jam’iyya don haka APCn take gani ba za ta yi wa jam’iyyar adalci ba.

Talla

A sanarwar da APCn ta fitar mai ɗauke da sa-hannun daraktan yaɗa labaran yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na Jam’iyyar Festus Keyamo ya yi watsi da naɗin Hajiya Naja’atu a matsayin mai lura da ayyukan ‘yan sanda a lokutan zaɓen ƙasar.

 

Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil

BBC Hausa ta rawaito Sanarwar da hukumar ‘yan sandan ta fitar ta ce ta maye gurbinta da tsohon mataimakin babban sifeton ‘yan sandan ƙasar Bawa Lawan domin lura da ayyukan ‘yan sanda a shiyyar ta arewa maso yamma.

 

Hukumar ta ce a kodayaushe tana taka-tsan-tsan a ayyukanta kuma za ta ci gaba da taimakawa wajen tabbatar da wanzuwar da dimokradiyya a ƙasar.

 

Haka kuma ta sake jaddada ƙudurinta na tabbatar da samun sahihin zaɓe a ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...