An kama malamin jinya kan zargin yi wa marasa lafiya fyaɗe

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

‘Yan sandan Uganda sun kama wani malamin jinya kan zargin yunkurin yi wa wasu mata masu ciki biyu fyaɗe a wani asibitin gwamnati mai suna Entebbe da ke da nisan kilomita 40 da Kampala, babban birnin ƙasar.

 

Mataimakin mai magana da yawun ‘yan sandan birnin, Luke Owoyesigire, ya ce an kama wanda ake zargin ne mai suna Kutesa Denis a jiya Lahadi kuma yana tsare a ofishin ‘yan sanda da ke Entebbe.

Talla

Ana zargin cewa sai da Kutesa ya bai wa matan biyu da ke sashin kula da mata na asibitin wani kwayar magani suka sha kafin ya ci zarafinsu.

 

Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil

An kuma gano wasu kwayoyi a gidansa bayan gudanar da bincike da kuma wata takarda da ake zargin ya rubuta inda yake rokon a yi masa addu’a kan abin da yake fuskanta mara kyau a yawan lokuta.

 

‘Yan sanda sun ce akwai yiwuwar ƙarin wasu da aka ci wa zarafi, inda suke buƙatar mutane su fito su yi magana.

 

Darektan asibitin, Dakta Peterson Kyebambe ya faɗa wa BBC cewa lamarin ya sanya yanzu sun fara saka ido kan likitoci da ma’aikata ko kuma kafa kyamarorin tsaro a faɗin asibitin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano Ta Kammala Aikin Gina Mayanka ta Naira Biliyan 1.5

Daga Zakaria Adam Jigirya     Gwamnatin jihar Kano ta karkashin Shirin...

An dakatar da Shugaba da Sakataren kungiyar APC X Eagle forum

Kwamitin zartarwa na kungiyar APC X Eagle forum ya...

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...