Yanzu-Yanzu :Ganduje ya Rushe Hukumar Remasab

Date:

Daga Sani Magaji Garko

Gwamnatin jihar Kano ta rushe hukumar kwashe shara da tsaftar Muhalli ta jihar Kano wato REMASAB.

Kwamishinan muhalli Dakta Kabiru Ibrahim Getso ne ya bayyana hakan yayin zantawarsa da ‘yan jaridu.

Ya ce gwamnatin Kano ta rushe hukumar, sai dai babu wani ma’aikaci ɗaya da zai rasa aikin sa, domin kuwa an yi tsarin rarraba ma’aikatan hukumar zuwa wasu hukumomin, su kuwa ma’aikatan wucin gadi an mikawa wani kamfanin Wanda suka sanya Hannu kan yarjejeniya da shi.

Ya ce, tuni gwamnati ta dauki matakin sauya salon sarrafa shara ta hanyar hadin guiwa da wani kamfani mai zaman kan sa da zai rika sarrafa shara, don ta zamo takin zamani da iskar gas da kuma wutar lantarki.

Kwamishinan ya ce kamfanin zai rika biyan gwamnati naira miliyan 50 a shekarar farko-farkon yarjejeniyar, a shekarun gaba Kuma ya rika biyan miliyan 100, haka zalika a shekarun karshen karshe na yarjejeniyar kamfanin zai rika biya naira miliyan 200 a duk wata.

kwamishinan muhalli
Getso ya kuma ce, kamfanin zai ɗauki ma’aikata sama da dubu hudu ciki har da injiniyoyi, kuma za su ninka albashin ma’aikatan da aka basu har sau uku.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gidauniyar Pyramid of Heart sun kai tallafin na’urar Oxygen Concentrated Asibitin Murtala dake Kano

Asibitin Ƙwararru na Murtala Muhd dake Kano ya yabawa...

Da dumi-dumi: ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU) ta dakatar da...

Ba mu da wata matsala da Ofishin mataimakin shugaban Kasa – NAHCON

Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ta karyata wani rahoto...

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nemi hukumar NBC ta fadada aikinta kan kafafen yada labarai na intanet

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci Hukumar...