Allah ya yi wa Sarkin Dutse, Nuhu Muhammad Sunusi rasuwa

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Allah ya yi wa Sarkin Dutse, Nuhu Muhammad Sunusi rasuwa.

Kwamishinan ayyuka na musamman a Jihar Jigawa Auwal Danladi Sankara ne ya tabbatar wa BBC da rasuwar sarkin.

Sarkin ya rasu ne ranar Talata a Abuja bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya kuma ya rasu yana da shekara 79.

Sakatare na musamman na marigayin Wada Alhaji Dutse ya tabbatar wa BBC cewa ana sa ran yin jana’izar sarkin ne a ranar Laraba a Dutse.

Kafin rasuwarsa, sarkin ya taɓa zama Uban Jam’iar Jihar Sokoto wato Sokoto State University.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...

Ana daf da yin jana’izar Aminu Dantata a Madina

Tawagar da gwamnatin Najeriya ta tura zuwa Madina na...