Karancin Man Fetur ka iya shafar zabe a Nigeria – INEC

Date:

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta a Najeriya INEC ta ce matsalar ƙaramncin man fetur da ƙasar ke fuskanta ka iya shafar tsare-tsaren hukumar game da za ta shirya zaɓen ƙasar da ke tafe.

Shugaban Hukumar Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka ranar Talata a Abuja a lokacin taron tuntuɓa tsakanin hukumar da ƙungiyoyin direbobin haya na ƙasar waɗanda suka haɗar da NARTO da NURTW da sauransu.

“Hukumar zaɓe tana tare da ku game da kokenku na ƙarancin man fetur da ƙasar nan ke fuskanta, da yadda hakan zai shafi hakar sufuri musamman a ranar zaɓe,” in ji Mahmood.

Ya ƙara da cewa “magana ta gaskiya ita ce rashin wadataccen man zai shafi shirye-shiryenmu”. Inji Farfesa Mahmoud

Talla

Shugaban hukumar ya ce dangane da wannan dalili , hukumar zaɓe za ta gana da kamfanin mai na ƙasa NNPCL domin duba hanyoyin da ya kamata a bi wajen magance wannan matsala.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...