Ganduje ya raba firjina na sama da Naira miliyan 12 ga Makarantun kwana

Date:

Daga Sani Abubakar Sani

 Ma’aikatar Ilimi ta jihar Kano ta saya tare da raba firjina Masu yin kankara Cikin sauri har na sama da Naira miliyan 12 ga Makarantun Kwana ga 38 a jihar Kano.


 Da yake jawabi yayin gabatar da injin daskarewa ga Shugabannin / Daraktocin Makarantun, Kwamishinan Ilimi, Malam Muhammad Sanusi Sa’id Kiru ya ce wannan karimcin ya zama dole da nufin taimakawa makarantun wajen kiyaye abinci musamman wadanda ke cikin saurin lalacewa.


 Ya kara da cewa, wannan shirin an yi shi ne don tallafawa ci gaban da ake samu a yanzu na inganta ciyarwa a makarantun Kwana a jihar Kano.


 Daga cikin 38 Freezers a cewar Kwamishinan, 37 za a raba su zuwa Makarantun Sakandare na kwana 37 yayin da Wanda ya rage za a bai wa makarantar yayan Yan Gudun Hijira da ke Mariri.


Cikin sanarwar da Jami’in Hulda da jama’a na Ma’aikatar Aliyu Yusuf ya go fitar yace kwamishinan ya bayyana cewa kudin da aka yi amfani da su wajen siyan Na’urorin sun samu ne daga kudaden da aka tara sakamakon aikin ciyarwar da aka sanya ido sosai.


 Yayi alkawarin binciko hanyoyin da za’a bi domin Samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana a Makarantu don tabbatar da samar da wutar lantarki a koda yaushe don aiki da firjin, ya bukaci shuwagabanin makarantun da yi amfani dasu da kuma kiyaye su.


 Hakazalika, kwamishinan ya nemi hadin kan su da kada su Bari ayi  wani mummunan aiki tare da ‘yan kwangilar da ke samar da kayan abinci ga makarantun su.


 Yayinda yake kuma nuna jin dadinsa ga irin goyon bayan da yawancin masu kula da makarantun ke bayarwa a cikin ingantaccen shirin ciyarwar, sai ya gargade su da su daina karbar kudi daga dalibai da sunan kudin da zasu yi Amfani dasu wajen siyan kayan aiki.


 Tun da farko, Babbar Sakatariyar ma’aikatar, Hajiya Lauratu Ado Diso ta bukaci shugabannin makarantar su guji tara muhimman bayanai da za a iya amfani da su wajen inganta ayyukan Makarantun su.


 Shugabannin / Daraktocin na Makarantun Sakandiren da ke kula da su gaba daya sun nuna godiyarsu tare da alkawarin yin amfani da firjinan da aka basu Kamar yadda ya dace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...