Gwamnatin Kano ta ayyana Talata, 1 ga Satumba, 2026, a matsayin ranar hutu domin bai wa al’ummar jihar damar gudanar da bikin Takutaha.
Sanarwar hakan tana kunshe ne cikin sanarwar da babban sakatare na Ma’aikatar Kafa Hukumomi, Abba A. Danguguwa, ya sanya wa hannu a madadin Shugaban Ma’aikatan Jihar.

A cewar sanarwar, ranar hutun ta yi daidai da 19 ga Rabi’ul Awwal, 1448AH, kuma Gwamna Abba Kabir Yusuf ne ya amince da ita.
Gwamnatin ta bayyana Takutaha a matsayin muhimmiyar al’ada da ke da matukar muhimmanci ga al’ummar Kano, tare da cewa bikin wani bangare ne na tarihin Musulunci a jihar.