Rundunar ‘Yan sandan Jihar Kano ta bayyana matakan tsaro da aka amince da su gabanin zaben cike gurbin ɗan majalisar Tarayya mai wakiltar Dawakin Kudu da Warawa wanda zai gudana ranar Asabar.
Wannan na ƙunshe cikin wata sanarwa da kakakin rundunar,CSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar.

Yace bisa umarnin kwamishina CP Ibrahim Adamu Bakori an takaita zirga-zirga a yankunan da za a gudanar da zaben daga karfe 12am zuwa ƙarfe 5pm a ranar Asabar, in banda jami’an da aka amince dasu.
Yace an tura isassun jami’an tsaro yankin domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi tare da sanya idanu kan yadda zaben zai gudana.
Sanarwar ta bukaci masu zabe su fito cikin lumana domin gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali.

Rundunar ta ayyana cewa ba za ta lamunci tashin hankalin zaɓe, siya ko sayar da ƙuri’a, kwace akwatunan zaɓe, tsoratar da masu zaɓe, da kuma yaɗa labarai na ƙarya ba.
Duk wanda aka samu yana aikata wani nau’in magudin zaɓe za a kama shi kuma a gurfanar da shi a gaban kuliya bisa ga Dokar Zaɓe ta 2022.