Gwamnatin Kano ta sanar da Ranar Fara hutun zangon Karatu na 3 ga ɗaliban jihar

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da ranar Juma’a 25 ga Yuli, 2025 a matsayin ranar da za a fara hutun zangon Karatu na 3 ga dukkan daliban makarantun kwana da makarantun firamare masu zaman kansu da na gaba da sakandare a jihar.

Don haka ana buƙatar iyayen da su je Makarantun ya’yansu don dauko ya’yansu da sanyin safiyar Juma’a 25 ga Yuli, 2025.

InShot 20250309 102512486
Talla

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar ilimi ta jihar Balarabe Abdullahi Kiru ya fitar .

Sanarwar ta bayyana cewa daliban makarantun kwana za su koma Makaranta a ranar Lahadi 7 ga watan Satumba 2025, yayin da daliban makarantun jekaka- dawo za su koma ranar Litinin 8 ga Satumba, 2025.

Gwamnatin Kano za ta fara jiyo ra’ayoyin al’umma kafin gudanar da duk wani aiki a jihar – Bilkisu Indabo

Kadaura24 ta ruwaito Kwamishinan Ma’aikatar Dakta Ali Haruna Makoda ya yi kira ga Iyaye da Dalibai da su tabbatar sun bin ka’idojin da aka amince da su na komawa Makarantun ya’yansu.

Dakta Makoda ya yi gargadin cewa za a dauki matakin ladabtarwa a kan daliban da suka karya dokokin komawa Makaranta.

Ya kuma godewa Iyayen yara bisa Hadin Kai da goyon baya da suke baiwa gwamnatin jihar Kano .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Fadar shugaban ƙasa ta mayar da martani ga Kalaman Kwankwaso

Fadar Shugaban Ƙasa ta musanta zargin Sanata Rabiu Musa...

Yadda Kwamishina a gwamnatin Kano ya tsayawa wani dilan ƙwaya aka bada belin sa a kotu

  Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Namadi, ya tsaya...

Kwankwaso ya caccaki gwamnatin Tinubu

  Tsohon gwamnan jihar Kano, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso ya...

Yanzu-yanzu: Jam’iyyar APC ta yi Sabon Shugabanta na Kasa

  Ministan Jinkai da ba da Agajin Gaggawa, Farfesa Nentawe...