SANARWA MUHIMMIYA (GABATAR DA SALLATUL GA’IB)
Assalamu Alaikum Warahmatullah,
Sakamakon rasuwa da Allah ya yiwa Alhaji Aminu Alhassan Dantata a Hadaddiyar Daular Larabawa a jiya Juma’a, Majalisar Malamai ta Kasa reshen Jihar Kano tana gayyatar daukacin al’umma domin halartar Sallatul Ga’ib na addu’ar rahama ga mamacin.

Za a gudanar da Sallatul Ga’ib din a yau, Asabar 28/06/2025, a Masallacin Umar Bin Khattab, dake Dangi, Kano, da misalin karfe 2:00 na rana.
Ana rokon al’umma da su hallarci wannan ibada domin neman rahamar Allah ga mamacin, tare da yi masa addu’ar samun gafara da jinƙai.
Allah ya jikansa, ya sanya Aljannah makomarsa.
Wassalamu Alaikum Warahmatullah.
Sanarwa:
Salisu Umar Gama,
A madadin Shugaban Majalisar Malamai,
Malam Ibrahim Khalil