Sanarwa ta Musamman daga majalisar malaman Kano game da rasuwar Dantata

Date:

SANARWA MUHIMMIYA (GABATAR DA SALLATUL GA’IB)

Assalamu Alaikum Warahmatullah,

Sakamakon rasuwa da Allah ya yiwa Alhaji Aminu Alhassan Dantata a Hadaddiyar Daular Larabawa a jiya Juma’a, Majalisar Malamai ta Kasa reshen Jihar Kano tana gayyatar daukacin al’umma domin halartar Sallatul Ga’ib na addu’ar rahama ga mamacin.

InShot 20250309 102512486
Talla

Za a gudanar da Sallatul Ga’ib din a yau, Asabar 28/06/2025, a Masallacin Umar Bin Khattab, dake Dangi, Kano, da misalin karfe 2:00 na rana.

Ana rokon al’umma da su hallarci wannan ibada domin neman rahamar Allah ga mamacin, tare da yi masa addu’ar samun gafara da jinƙai.

Allah ya jikansa, ya sanya Aljannah makomarsa.

Wassalamu Alaikum Warahmatullah.

Sanarwa:
Salisu Umar Gama,
A madadin Shugaban Majalisar Malamai,
Malam Ibrahim Khalil

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Alhaji Aminu Dantata ta bar gibin da zai yi wuyar cikewa a Nigeria – Alhaji. Kabiru Sani Kwangila

Shugaban kamfanin gine-gine na SKY Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Aminu Dantata ya bar mana wasiyyar inda za a binne shi – Iyalansa

Iyalan marigayi Alhaji Aminu Alassan Dantata sun shaida cewa...

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...