Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala Sule Garo, ya taya daukacin al’ummar Musulmi barka da shigowar sabuwar shekarar Musulunci ta 1447 bayan Hijira.
A cikin sakon taya murna da ya fitar a ranar Litinin, Garo ya bayyana ranar 1 ga Muharram a matsayin lokaci mai matukar muhimmanci a duniyar Musulunci, wanda ke tunatar da darussan hijirar Manzon Allah (SAW) daga Makkah zuwa Madina da darussa na imani, jajircewa, da sadaukarwa.

Ya bukaci Musulmai da su yi amfani da wannan lokaci wajen karfafa kaunar juna, tausayi da jinkai a tsakanin al’umma, tare da jajircewa wajen gina zaman lafiya da hadin kai.
Yadda Makarantar JSS Unguwa uku dake K/H Tarauni ta Zama mafakar shaye-shaye da yan daba
“Dukkan mu akwai rawar da za mu iya takawa don gina al’umma da tabbatar da zaman lafiya, kamar yadda addinin Musulunci ya koyar da mu,” in ji Garo.
Ya kuma yi addu’ar neman albarka da zaman lafiya a jihar Kano da Najeriya baki daya, tare da fatan Allah ya sanya sabuwar shekarar ta Musulunci ta kasance ta kawo wanzuwar zaman lafiya da arziki a jihar Kano da Kasa baki daya.
Barka da Sabuwar Shekarar Hijira!