Daga Rukayya Abdullahi Maida
Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusif, ya ba da umarnin a gaggauta gyara makarantar koyon harsunan Faransanci da Sinanci mallakar gwamnatin jihar, a ƙoƙarinsa na bunƙasa ɓangaren ilimi da inganta koyo da koyarwa a jihar Kano
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwarwa da kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ya sanyawa hannu kuma ya aikowa Kadaura24.
Sanarwar ta ce umarnin gwamnan ya biyo bayan wata ziyarar bazata da ya kai makarantar da ke garin Kwankwaso, a ƙaramar hukumar Madobi a farkon makon nan.

A cewar Gwamnan, “Na kai ziyara makarantar ne domin na ganewa idanuna yadda ɗalibai da malamai ke gudanar da harkokinsu, da kuma yanayin gine-ginen makarantar”.
Gwamnan ya bayyana jin daɗinsa bisa ƙwazon malamai da ɗaliban, musamman yadda ɗaliban ke iya magana da kyau da harsunan Faransanci da Sinanci.
Iyalan mafarautan da aka kashe a Edo sun zargi gwamnatin kano da yin watsi da su
“Za mu gyara makarantar ba tare da ɓata lokaci ba, adon haka na umarci Kwamishinan aiyuka da ya hanzarta fara aikin gyaran gine-ginen da suka lalace a makarantar”.
sanarwar ta ce wannan mataki na daga cikin tsare-tsaren gwamnatin Kano, na inganta ilimi da samar da ingantacciyar nagarta a fannin koyon harsuna domin bunƙasa ci gaban jihar.