Gwamna Abba ya ba da Umarnin gyara makarantar koyon harsunan Faransanci da Chananci dake Kano

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusif, ya ba da umarnin a gaggauta gyara makarantar koyon harsunan Faransanci da Sinanci mallakar gwamnatin jihar, a ƙoƙarinsa na bunƙasa ɓangaren ilimi da inganta koyo da koyarwa a jihar Kano

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwarwa da kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ya sanyawa hannu kuma ya aikowa Kadaura24.

Sanarwar ta ce umarnin gwamnan ya biyo bayan wata ziyarar bazata da ya kai makarantar da ke garin Kwankwaso, a ƙaramar hukumar Madobi a farkon makon nan.

InShot 20250309 102512486
Talla

A cewar Gwamnan, “Na kai ziyara makarantar ne domin na ganewa idanuna yadda ɗalibai da malamai ke gudanar da harkokinsu, da kuma yanayin gine-ginen makarantar”.

Gwamnan ya bayyana jin daɗinsa bisa ƙwazon malamai da ɗaliban, musamman yadda ɗaliban ke iya magana da kyau da harsunan Faransanci da Sinanci.

Iyalan mafarautan da aka kashe a Edo sun zargi gwamnatin kano da yin watsi da su

“Za mu gyara makarantar ba tare da ɓata lokaci ba, adon haka na umarci Kwamishinan aiyuka da ya hanzarta fara aikin gyaran gine-ginen da suka lalace a makarantar”.

sanarwar ta ce wannan mataki na daga cikin tsare-tsaren gwamnatin Kano, na inganta ilimi da samar da ingantacciyar nagarta a fannin koyon harsuna domin bunƙasa ci gaban jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

  Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...